Matuka marigayi Sheikh Giro ya gyara tarbiyyar al’umma a wa’azinsa – Buhari

0

Tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan Sheikh Abubakar Giro Argungu sakamakon rasuwarsa bayan gajeriyar jinya a ranar Laraba.

Independent Mirror ta rawaito cewa a Ranar Alhamis ne da aka gudanar da jana’izar marigayi Sheikh Giro wanda al’umma da dama suka halarta.

“Ina miƙa ta’aziyyata ga iyalai da mabiyansa,” a cewar Buhari.

Shugaba Buhari ya kuma ce yana mai addu’ar “Allah ya ji ƙan sa, ya saka shi cikin Jannatul-Firdaus”.

“Matuka ya tsaya kan ɗabi’un Musulunci tare da nuna jajircewarsa a aikace wajen gyara tarbiyyar al’umma ta hanyar wa’azinsa da ayyukansa.”

A ranar Alhamis aka yi jana’izar malamin a masallacin Idi na garin Argungu da ke jihar Kebbi, inda dubban mabiyansa suka halarci binne shi.

BBC

Leave A Reply

Your email address will not be published.